Saudiyya Tabada Daman Zuwa Umrah.


 

Mahukunta a Saudiyya suna sanar cewa za a kyale mazauna ƙasar su gudanar da ayyukan ibada na Umrah bayan ta dakatar da ita na tsawon watanni.

Hukumomin ƙasar sun ce daga baya za su kyale maniyyata daga ƙasashen waje su shiga ƙasar domin gudanar da ibadar wadda take da muhimmanci ga Musulmin duniya, sai dai za ta ƙayyade yawan maniyyatan da yawan ƙasashen da za ta bari su shiga ƙasar.

Maniyatta da ke cikin Saudiyya na iya yin Umrah daga ranar 4 ga watan Oktoba, inda maniyattan da ke ƙasashen ƙetare kuwa sai sun jira zuwa ranar 1 ga watan Nuwamba kafin su sami izinin shiga ƙasar.

Ma'aikatar Aikin Hajji ta Saudiyya ta kuma bayyana cewa idan annobar korona ta gushe, za ta kyale dubban maniyatta daga ko'ina a duniya su ci gaba da ziyartar biranen Makkah da Madin domin gudanar da ibadunsu.

No comments:

Post a Comment

Adbox